Kamfanin Dillancin Labaran Hauza ya ruwaito cewa, Hujjatul Islam Jawad Muhaddithi, malami a Hauza da Jami'a, ya yi bitar mafi fice daga cikin falalolin Amirul Muminina (A.S) a cikin Ziyarar Ghadir, wanda ake gabatar muku da shi:
Bismillahir Rahmanir Rahim
Sallama da gaisuwa da fatan alheri gare ku manyan mutane; muna taya murna ta musamman saboda shigowar kwanakin Wilaya da bukukuwan Ghadir. Muna farin ciki da kasancewarmu mabiya Maula Ali (A.S), kuma soyayyarsa da ta zuriyarsa tana cikin zukatanmu da na iyalanmu.
Mu a lokuta da dama, muna tunawa da Imam Ali al-Naqi, Imam Hadi (A.S) na musamman; daya a ranar haihuwarsa, daya a ranar shahadarsa, daya kuma a ranar Ghadir inda aka ruwaito Ziyarar Ghadir daga gare shi, sannan kuma a cikin wurare masu tsarki daban-daban, lokacin da muke karanta Ziyarar Jami'at al-Kabira.
Imam Hadi (A.S); Jagoran Bayyana Matsayin Ahlul-Bait (A.S)
Da farko, bari in bayyana cewa ziyara, a cikin al'adunmu na 'yan Shi'a, wani babi ne da dama ta sanin alfahari, ayyuka, da falalolin Ahlul-Bait (A.S). Wato, A'imma ma'asumai (A.S) a cikin ziyarori da aka samo daga gare su, sun bayyana manyan koyarwa na gaskiyar Shi'anci da madaukakan ilimi a gare mu.
Musamman ma, muna da bashin Imam Hadi (A.S). A wannan bangare, muna da ziyarori guda biyu masu girma, fadi, cike da bayanai, kuma cikakku wadanda duka an ruwaito su ne daga Imam Hadi (A.S); daya ita ce Ziyarar Jami'at al-Kabira, wacce za a iya ziyartar kowane Imami da ita, kuma an yi kwadaitarwa a kanta. Wannan ziyara, tarin ilimi ne da ya shafi Shi'a, a zahiri sanin Shi'a, sanin Imama, da sanin Imami ne. Daya daga cikin mafi muhimmanci, ingantattu, kuma cikakkun majiyoyi na sanin matsayin Imami, Wilaya da Ahlul-Bait (A.S) ita ce Ziyarar Jami'at al-Kabira wacce aka ruwaito daga Imam Hadi (A.S).
Dayar kuma ita ce ziyarar Amirul Muminina (A.S) a ranar Idil Ghadir wacce take da tsawo sosai. Dubi cikin littafin Mafatihul Jinan; ziyarar Hazrat Amir (A.S) a ranar Ghadir ita ma an ruwaito ta ne daga harshe mai albarka na Imam Hadi (A.S).
A gaskiya, ga wadanda suke adawa da Ahlul-Bait kuma suke sahun gaba wajen gaba da gaskiya, fuskantar wadannan manyan tarukan guda biyu – wanda daya sanin A'imma da Ahlul-Bait (A.S) ne, dayar kuma sani na musamman ne ga Ali (A.S) da falalolinsa – yana da matukar wahala da nauyi. Don haka ne ma, Nasibawa da masu adawa da Ahlul-Bait (A.S) suke da ƙiyayya ta musamman da Imam Hadi (A.S).
Idan kuna tunawa, a shekarun baya har ma ta hanyar amfani da zanen barkwanci, fina-finai, da cin mutunci da suke yi a tsakanin A'imma (A.S) ga Imam Hadi (A.S), watakila hakan ya faru ne saboda radadin da suka ji daga bayanin wannan bawan Allah da kuma fafutukar bayyanawa (Jihad al-Tabyin) ta Imam Hadi (A.S); domin a cikin dukkan wadannan ziyarori guda biyu masu zurfi da daukaka, an bayyana ainihin fuskar gaskiya ta Ahlul-Bait da A'imma ma'asumai (A.S), musamman Ali (A.S) a ziyarar ranar Ghadir.
Ziyarar Ghadir; Kundin Falaloli da Darajojin Amirul Muminina (A.S)
Ziyarar Amirul Muminina (A.S) a ranar Idil Ghadir, cikakken jerin sunaye ne na lakabobi, falaloli da matsayi na Hazrat Amir (A.S) da rawar da ya taka wajen kare Musulunci; hadisai da aka ruwaito daga harshe mai albarka na Manzon Allah (S.A.W.A) game da shi, ayoyin Alƙur'ani masu girma wadanda suka sauka game da Amirul Muminina (A.S) kuma kamar yadda riwayoyi suka nuna, sababin saukarsu falala ce, matsayi da aikin Ali (A.S), sannan kuma yakukuwa da muhimman abubuwan da suka faru a tarihin Musulunci inda Ali (A.S) ya taka rawa. Dukkan wadannan an kawo su ne ta hanya mai fadi, mai daukar hankali, kuma da gaske mai ban mamaki a cikin ziyarar Amirul Muminina (A.S) a ranar Idil Ghadir.
Yin bayani da fashin baki kan wannan ziyara yana daukar lokaci mai tsawo kuma yana bukatar zama mai yawa; amma gwargwadon damar da muke da ita, zan yi bitar wasu sassa na wannan ziyara a gabanku masoya.
Farkon wannan ziyara a cikin Mafatihul Jinan yana farawa kamar haka:
«السَّلَامُ عَلَی مُحَمَّدٍ رَسُولِ اللَّهِ، خَاتَمِ النَّبِیِّینَ وَسَیِّدِ الْمُرْسَلِینَ وَصَفْوَةِ رَبِّ الْعَالَمِینَ»
"Aminci ya tabbata ga Muhammad Manzon Allah, cikamakon Annabawa, shugaban manzanni, kuma zababban Ubangijin halittu."
Wannan sashe yana bayyana falalolin Annabi ne da gaisuwa ta musamman ga Manzo, Annabi mai girma (S.A.W.A).
A sashe na gaba yana cewa:
«السَّلَامُ عَلَی أَنْبِیَاءِ اللَّهِ وَرُسُلِهِ وَمَلَائِکَتِهِ الْمُقَرَّبِینَ وَعِبَادِهِ الصَّالِحِینَ»
(Aminci ya tabbata ga Annabawan Allah da Manzanninsa da Mala'ikunsa na kusa da bayinsa salihai)
Gaisuwa da salati ga Annabawan Allah, mala'iku na kusa da Ubangiji da bayinsa salihai.
Bayan haka, sai a shiga gaisuwa da girmamawa ga Amirul Muminina (A.S):
Kamar yadda na fada, dukkan kalmomin wannan doguwar ziyara suna bayyana falaloli da darajojin Maula (A.S) kuma suna bukatar bayani. Hujjojin kowace kalma da jimla a cikin wannan suna nan a cikin riwayoyinmu da kuma majiyoyi daban-daban; amma a cikin wannan ziyara, an tattara su wuri guda kuma an bayyana su daga harshen Imam Hadi (A.S).
An bayyana Amiral Muminina (A.S) a matsayin shugabanmu kuma shugaban muminai; wanda shi ne:
«أَمِینُ اللَّهِ فِی أَرْضِهِ وَصَفِیُّهُ فِی خَلْقِهِ» (Aminin Allah a bayan kasa kuma zababben Sa a cikin halittun Sa).
- Shi ne hujjar Ubangiji a kan bayi.
- Shi ne addini tsayayye na Allah kuma tafarki madaidaici na Ubangiji. Babu wani tafarki madaidaici in ban da Ali (A.S).
«السَّلَامُ عَلَیْکَ أَیُّهَا النَّبَأُ الْعَظِیمُ الَّذِی هُمْ فِیهِ مُخْتَلِفُونَ»
(Aminci ya tabbata a gare ka ya kai Babban Labari wanda suke sabani a kansa)
Wannan yana ishara ne ga hadisai da suka zo wajen sababin saukar suratu Naba'i (Amma), cewa wannan "Babban Labari" wanda mutane suke tambaya a kansa kuma suke magana a kansa, har wasu ma suna sabani a kansa, an fassara shi da samuwar Ali (A.S).
Aminci ya tabbata gare ka ya Amiral Muminina; a lokacin da mutane suka kasance masu shirka, kai ka yi imani; «وَصَدَّقْتَ بِالْحَقِّ وَهُمْ مُکَذِّبُونَ» (Kuma ka gasgata gaskiya a lokacin da suke karya tawa); yayin da wasu suke karyata shi, kai mai gasgata gaskiya ne, kuma «وَجَاهَدْتَ وَهُمْ مُحْجِمُونَ» (Kuma ka yi yaki a lokacin da suke ja da baya); a lokacin da wasu suke gudu daga fagen fama, gwagwarmaya da kare gaskiya, Hazrat Amir ya kasance mayaki ne.
«مُخْلِصًا لِلَّهِ الدِّینَ، صَابِرًا مُحْتَسِبًا حَتَّی أَتَاکَ الْیَقِینُ»
(Kuna masu tsarkake addini ga Allah, kuna masu hakuri da neman lada har sai da mutuwa ta zo muku)
Rayuwa guda ta bauta ta gaskiya da mika wuya cikin ikhlasi har lokacin da ajalinsa da shahadarsa ta zo.
«السَّلَامُ عَلَیْکَ یَا سَیِّدَ الْمُسْلِمِینَ وَیَعْسُوبَ الدِّینِ وَیَعْسُوبَ الْمُؤْمِنِینَ وَإِمَامَ الْمُتَّقِینَ وَقَائِدَ الْغُرِّ الْمُحَجَّلِینَ»
(Aminci ya tabbata a gare ka ya shugaban musulmai, kuma jagoran addini, kuma jagoran muminai, kuma shugaban masu tsoron Allah, kuma jagoran fararen fuskoki [masu haske a ranar kiyama])
Wadannan duka suna daga cikin siffofin Hazrat Amir (A.S).
«أَشْهَدُ أَنَّکَ أَخُو رَسُولِ اللَّهِ وَوَصِیُّهُ وَوَارِثُ عِلْمِهِ وَأَمِینُهُ عَلَی شَرْعِهِ»
(Ina shaidawa cewa lallai kai dan uwan Manzon Allah ne, kuma wasiyyinsa, kuma magajin iliminsa, kuma amininsa a kan shari'arsa)
Ina shaidawa cewa kai dan uwan Manzon Allah ne, wasiyyin Annabi ne, magajin ilimin sa ne, amini ne a kan shari'arsa, halifan Annabi ne a cikin al'ummarsa, kuma «أَوَّلُ مَنْ آمَنَ بِاللَّهِ وَصَدَّقَ بِمَا أُنْزِلَ عَلَی نَبِیِّهِ» (Farkon wanda ya yi imani da Allah kuma ya gasgata abin da aka saukar wa Annabinsa).
Ina shaidawa cewa Annabi ya isar da abin da aka wajabta masa daga wajen Allah na isarwa; ya bayyana kiran sa a bayyane kuma ya wajabta wa al'umma su yi biyayya ga Annabi da Wilayarsa, kuma ya karbi bai'a daga mutane a kan wannan gaskiya, kuma ya sanya ka, ya Ali, ka fi muminai iko da kawunansu fiye da yadda suke da shi.
Wannan yana nuni ne ga hudubar Ghadir ta Annabi mai girma (S.A.W.A) inda ya ce:
أَلَسْتُ أَوْلَی بِکُمْ مِنْ أَنْفُسِکُمْ؟»
(Shin ban fi ku iko da kawunanku ba?)
Duka suka ce: "Kwarai kuwa ya Manzon Allah". Sai ya ce: «مَن کنتُ مولاه فهذا علی مولاه».
(Duk wanda na kasance shugabansa ne, to wannan Ali shugabansa ne)
Kuma Allah ya shaida cewa Annabi ya sauke wannan sako kuma ya fadi wannan huduba mai ratsa jiki a Ghadir Khum, kuma hujja ta cika a kan kowa.
«وَلَعَنَ اللَّهُ جَاحِدَ وِلَایَتِکَ بَعْدَ الْإِقْرَارِ، وَنَاکِثَ عَهْدِکَ بَعْدَ الْمِیثَاقِ»
(Kuma Allah ya la'anci mai musun Wilayarka bayan ya amince, da mai karya alkawarinka bayan an yi yarjejeniya)
La'anar Allah ta tabbata ga wanda bayan ya amince da Wilayarka da kuma bayan alkawari da yarjejeniya da ya kulla da kai a ranar Ghadir, ya musanta Wilayarka.
A Ghadir, mutane sun zo sun yi bai'a ga Amirul Muminina (A.S) a matsayin shugaban muminai, sun gaisa da shi kuma sun halarci waccan gagarumar liyafa da aka gudanar a Ghadir har tsawon kwanaki uku a jere. Wadanda bayan haka suka karya alkawari, suka saba yarjejeniya kuma suka musanta Wilayar wancan bawan Allah, suna karkashin la'anar Ubangiji.
«أَشْهَدُ أَنَّکَ أَمِیرُ الْمُؤْمِنِینَ حَقًّا لم تنطق بولایتک التنزیل»
(Ina shaidawa cewa kai ne shugaban muminai na gaskiya, wanda Alkur'ani ya yi magana da Wilayarka)
Ina shaidawa cewa kai ne shugaban muminai; kai ne waccan gaskiya wacce Alkur'ani da wahayi suka yi magana a kan Wilayarka, kuma Allah da Manzonsa sun dauki alkawari da yarjejeniya daga al'umma a kan Wilayarka.
Ina shaidawa cewa kai da baffanka Hamza Sayyidus Shuhada, da dan uwanka Ja'afar bin Abi Talib (Ja'afar al-Tayyar), kuna cikin wadanda suka sayar da rayukanku ga Allah; kun kare Musulunci da addinin Allah da rayukanku, kuma wannan aya ta sauka game da ku:
«إِنَّ اللَّهَ اشْتَرَی مِنَ الْمُؤْمِنِینَ أَنْفُسَهُمْ وَأَمْوَالَهُمْ بِأَنَّ لَهُمُ الْجَنَّةَ»
(Lallai Allah ya saya daga muminai rayukansu da dukiyoyinsu da cewa suna da gidan Aljanna)
Har zuwa karshen ayar da take bushara ta Ubangiji ga wadanda suka sadaukar da rayukansu saboda gaskiya, addinin Annabi da Musulunci, kuma «ذَٰلِکَ هو الْفَوْزُ الْعَظِیمُ» (Wannan shi ne rabo mai girma).
Aya tana cewa:
«التَّائِبُونَ الْعَابِدُونَ الْحَامِدُونَ السَّائِحُونَ الرَّاکِعُونَ السَّاجدُونَ»
(Masu tuba, masu bauta, masu godiya, masu azumi, masu ruku'u, masu sujada)
Kamar yadda hadisai suka nuna, mafi bayyanar misali a kanta shi ne Ali (A.S).
Ina shaidawa, ya Amiral Muminina, cewa wanda ya yi shakka a kanka da kuma a kan Imamancinka da Wilayarka, bai yi imani da Manzo amintacce ba, kuma wanda ya gabatar da wani a kanka, ya fita daga tsayayyen addinin Allah; addinin da Allah ya yarda wa mutane kuma ya ce:
«وَرَضِیتُ لَکُمُ الْإسْلَامَ دِینًا»
(Kuma na yarda muku da Musulunci ya zama addini)
Allah wanda ya cika addininsa da Wilayarka a ranar Ghadir.
Ina shaidawa, ya Ali, cewa kai ne wanda Allah mabuwayi mai jinkai ya ce game da shi:
«وَأَنَّ هَذَا صِرَاطِی مُستَقِیمًا فَاتَّبِعُوهُ»
(Kuma lallai wannan shi ne tafarki na madaidaici, to ku bi shi)
Nufin wannan tafarki madaidaici shi ne kai, kuma wannan aya ta sauka ne a kan matsayinka, kuma Annabi ya la'anci wadanda suka kauce daga gare ka da gaskiyarka suka kama wata hanya daban.
Wannan ziyara tana ci gaba har sai ta kai ga wannan sashe:
«أَشْهَدُ أَنَّکَ لَمْ تَزَلْ لِلْهَوَی مُخَالِفًا وَلِلتُّقَی حَلِیفًا وَعَلَی کَظْمِ الْغَیْظِ قَادِرًا»
(Ina shaidawa cewa ba ka gushe ba kana mai sabawa son rai, kana abokin tsoron Allah, kuma kana mai iya hadiye fushi)
Ina shaidawa cewa kai kullum kana sabawa son rai, kana tare da tsoron Allah, kana da ikon hadiye fushi, kana da ikon yafe wa mutane, kuma duk lokacin da aka saɓa wa Allah kana yin fushi, kuma duk lokacin da aka yi masa biyayya kana yin farin ciki.
Ka yi aiki da abin da Allah ya kulla alkawari da kai, ka kiyaye abin da aka dora maka na kariya, ka amince da amanar Allah da Manzo, ka isar da abin da aka dora a kafadarka, kuma ka jira abin da aka yi maka alkawari.
«وَأَشْهَدُ أَنَّکَ مَا بَرِحْتَ فِی الْحَقِّ سَاعِیًا وَعَنِ الْحَقِّ غَیْرَ وَانٍ»
(Kuma ina shaidawa cewa ba ka gushe ba kana mai kokari a cikin gaskiya, kuma ba ka taba kasala ba daga barin gaskiya)
Ina shaidawa cewa kai kullum kana kan hanyar gaskiya, ba ka rabu da gaskiya ba, kuma ba ka yi kasa a gwiwa ba wajen kare gaskiya. Ba ka taba yin sulhu ko nuna rauni ba a cikin addinin Allah da yardarsa.
Kariyar Allah ga hakan ya kasance akasin haka; a'a, kai koda an zalunce ka, ka jure wa wadancan zalunci saboda Allah kuma ka mika al'amarinka ga Allah.
Ina shaidawa, ya Ali, ya Amiral Muminina, cewa «جَاهَدْتَ فِی اللَّهِ حَقَّ جِهَادِهِ» (Ka yi yaki a cikin Allah yaki na gaskiya); kamar yadda ya kamata ka yi gwagwarmaya a tafarkin Allah har lokacin da Allah ya neme ka zuwa kusa da Shi, kuma da zabinsa ya karbi kwan ka kuma ya cika hujja a kan makiyanka, ka zama cikakkiyar hujja a kan kowa.
Aminci ya tabbata a gare ka, ya shugaban muminai; wanda ka bauta wa Allah cikin ikhlasi, ka yi yaki a tafarkin Allah cikin hakuri, ka sadaukar da rayuwarka saboda addinin Allah, ka yi aiki da littafinsa, ka bi sunnar Annabinsa, «أَقَمْتَ الصَّلَاةَ وَآتَیْتَ الزَّکَاةَ وَأَمَرْتَ بِالْمَعْرُوفِ وَنَهَیْتَ عَنِ الْمُنْکَرِ» (Ka tsayar da sallah, ka bada zakka, ka yi umarni da kyakkyawa, ka yi hani da mummuna).
Kamar yadda na fada, wadannan falaloli suna ci gaba, kuma duk abin da Amirul Muminina (A.S) ya nuna na jajircewa, fafutuka, ikhlasi da tsayin daka a duk tsawon rayuwarsa da kuma a wurare daban-daban na tarihin Musulunci, ana ci gaba da kawo su a cikin sassa da jimlolin wannan ziyara domin kada mu manta da abin da aka fada game da shi a farkon Musulunci.
«أقسم بالله قَسَمَ صِدق ...» (Ina rantsuwa da Allah rantsuwa ta gaskiya...)
Ina rantsuwa da Allah rantsuwa ta gaskiya cewa Annabi da iyalansa, wadanda amincin Allah ya tabbata a gare su, su ne shugabannin halittu, kuma kai ne shugaba na da shugaban muminai. Kai bawan Allah ne, waliyin Allah ne, dan uwan Manzon Allah ne, wasiyyinsa ne kuma magajinsa ne.
Kai ne wanda Annabi ya ce game da shi:
«وَالَّذِی بَعَثَنِی بِالْحَقِّ مَا آمَنَ بِی مَنْ جَحَدَکَ»
(Ina rantsuwa da wanda ya aiko ni da gaskiya, bai yi imani da ni ba wanda ya musanta ka)
Kuma duk wanda ya rabu da kai, ya bata kuma bai bi madaidaiciyar hanya ba.
Ina shaidawa cewa kai ne hujjar Allah a kan bayi, mai shiyarwa zuwa ga hanyar girma, kuma mai nuna hanya zuwa ranar kiyama.
Ubangiji madaukaki bai gushe ba yana daukaka sunanka da matsayinka:
«رفع الله فی أولی منزلتک و أعلی فی الآخرة درجتک».
(Allah ya daukaka matsayinka a farko [duniya], kuma ya daukaka darajarka a karshe [lahira]).
«ولعن الله مستحل الحرمة منک و السالب لک حقک».
(Kuma Allah ya la'anci mai halatta alfarmarka da mai kwace maka hakki).
Ina shaidawa cewa su ne mafi asarar mutane wadanda za a jefa su a cikin wuta ranar kiyama a kife a kan fuskokinsu.
Ya Ali, ina shaidawa cewa kai ne bayyananniyar hanya da haske mai haskakawa, kuma a inda Ubangiji madaukaki ya ce:
«هَلْ یَسْتَوِی الَّذِینَ یَعْلَمُونَ وَالَّذِینَ لَا یَعْلَمُونَ»
(Shin wadanda suka sani suna daidai da wadanda ba su sani ba?)
Kai ne mafi bayyanar misali na «الذین یَعلمون» (Wadanda suka sani).
Kai ne wanda ya kare addinin Allah da Manzon Allah. Alkur'ani yana magana dangane da falalarka. A inda Allah yake cewa:
«فَضَّلَ اللَّهُ الْمُجَاهِدِینَ عَلَی الْقَاعِدِینَ أَجْرًا عَظِیمًا»
(Allah ya daukaka masu yaki a kan masu zama da lada mai girma)*
Wannan game da kai ne.
Kuma a inda yake cewa:
«أَجَعَلْتُمْ سِقَایَةَ الْحَاجِّ وَعِمَارَةَ الْمَسْجِدِ الْحَرَامِ کَمَنْ آمَنَ بِاللَّهِ وَالْیَوْمِ الْآخِرِ وَجَاهَدَ فِی سَبِیلِ اللَّهِ»
(Shin kun sanya shayar da mahajjata da gina masallaci mai alfarma kamar wanda ya yi imani da Allah da ranar kiyama kuma ya yi yaki a tafarkin Allah?)
Kai ne mafi bayyanar misali a kansa.
Kuma a inda yake cewa:
«الَّذِینَ آمَنُوا وَهَاجَرُوا وَجَاهَدُوا فِی سَبِیلِ اللَّهِ بِأَمْوَالِهِمْ وَأَنْفُسِهِمْ أَعْظَمُ دَرَجَةً عِنْدَ اللَّهِ»
(Wadanda suka yi imani suka yi hijira kuma suka yi yaki a tafarkin Allah da dukiyoyinsu da rayukansu, suna da daraja mai girma a wajen Allah). Mun yi itfakin wannan shi ma kai ne.
Ya Ali, kai ne wanda lokacin da Annabi mai girma (S.A.W.A) aka umarce shi daga wajen Allah da ya bayyana Wilayarka, kuma Allah ya ce: «بلغ ما أُنزل إلیک من ربک...» (Ka isar da abin da aka saukar maka daga Ubangijinka...)
Annabi ya yi umarni da a shirya mimbari daga kayan dawakai da raƙuma, ya daga hannunka kuma ya bayyana kiran Allah da buƙatar Allah ga mutane.
A cikin waccan doguwar huduba ya ce:
«ألستُ أولی بِکم مِن أَنفسکم؟»
(Shin ban fi ku iko da kawunanku ba?) Duka suka ce:
"Ya Allah, kwarai kuwa".
A lokacin sai ya kama hannun Ali ya ce:
«اللَّهُمَّ وَالِ مَنْ وَالَاهُ وَعَادِ مَنْ عَادَاهُ وَانْصُرْ مَنْ نَصَرَهُ وَاخْذُلْ مَنْ خَذَلَهُ».
(Ya Allah ka so wanda ya so shi, ka yi gaba da wanda ya yi gaba da shi, ka taimaki wanda ya taimaki shi, ka tozarta wanda ya tozarta shi)
Akwai sauran ayoyi ma a cikin Alkur'ani mai girma da sun sauka ne a kan matsayin Ali (A.S). Yana nuni da saukar suratul "Hal Ata" (Suratul Insan) yana cewa:
«و یطعمون الطعام علی حبه مسکیناً و یتیماً و أسیراً»
(Kuma suna ciyar da abinci saboda sonsa ga matalauci da maraya da kamamme (ribar yaƙi)
Domin neman yardar Allah ka ba da abinci ga matalauci, maraya, da kamamme.
"Wane ne in ban da Ali zai gaya wa dansa cewa: tunda makashi na yana hannunka, yanzu ka kyautata masa?"
Kai ne kake da waccan falala:
«وَلَا نُرِیدُ مِنْکُمْ جَزَاءً وَلَا شُکُورًا»
(Ba ma neman wani sakamako ko godiya daga gare ku)
Kuma Allah ya saukar da wadannan ayoyi a kan hakkinka.
Haka kuma:
«وَیُؤْثِرُونَ عَلَی أَنْفُسِهِمْ وَلَوْ کَانَ بِهِمْ خَصَاصَةٌ»
(Kuma suna fifita wasu a kan kawunansu koda kuwa suna da bukata)
Ko da su da kansu suna da bukata, suna gabatar da wasu a kan kansu kuma suna sadaukarwa. Wannan a kan haƙƙinka ne, ya Ali (A.S).
Kuma a inda Allah yake magana game da masu hakuri a cikin tsanani da masu tsayin daka a fagen fama, kai ne mai hakuri a yakin da tsanani.
Kai ne wanda Annabi ya ce game da shi:
«عَلِیٌّ یَقْسِمُ بِالسَّوِیَّةِ وَیَعْدِلُ فِی الرَّعِیَّةِ»
(Ali yana raba dukiya cikin daidaito kuma yana yin adalci a cikin talakawa)
Kai ne mai wurare sanannu, matsayi shahararre, da kwanaki ambatattu; kwanaki da ba za a taba mancewa da su ba wadanda ka taka rawa a cikinsu; ranar Badar, ranar Ahzab da wancan matsayi inda:
«زَاغَتِ الْأَبْصَارُ وَبَلَغَتِ الْقُلُوبُ الْحَنَاجِرَ»
(Idanu suka karkata kuma zukata suka kai ga makogwaro)
Duk idanu suna cikin damuwa, zukata sun kai ga makogwaro kuma mutane sun fara tunani daban-daban game da Allah.
Wani rukuni yana tunanin cewa alkawuran Ubangiji ba za su cika ba, kuma:
«وَزُلْزِلُوا زِلْزَالًا شَدِیدًا»
(Kuma aka girgiza su girgizawa mai tsanani)
Mutane da yawa sun girgiza.
Munafukai da masu rashin lafiya a zukata suna cewa:
«مَا وَعَدَنَا اللَّهُ وَرَسُولُهُ إِلَّا غُرُورًا»
(Abin da Allah da Manzonsa suka yi mana alkawari ba komai ba ne face yaudara)
Kuma munafukai da suke cewa:
«یَا أَهْلَ یَثْرِبَ لَا مُقَامَ لکُمْ فَارْجِعُوا»
(Ya ku mutanen Madina babu wurin zama gare ku, don haka ku koma)
Kada ku zauna a Madina, ku koma; aikin Musulunci ya kare.
Wasu kuma suna neman izini daga Annabi don barin yaki suna cewa:
«إِنَّ بُیُوتَنَا عَوْرَةٌ»
(Lallai gidajenmu a bude suke [ba su da kariya])
Amma a cikin dukkan wadannan bukukuwa da matsorata da masu raunin imani suke neman gudu daga halaka, ya Ali, kai ne ka tsaya, ka jure, ka yi yaki, ka buga takobi, kuma Musulunci ya ci gaba da karfin yaki da takobinka.
Zan takaita da wannan gwargwado. Watakila abubuwan da na nuna, ba su kai ko kashi daya cikin uku na falaloli da darajojin da aka bayyana a cikin wannan ziyara cikakka ba, wato ziyarar Amiral Muminina (A.S) a ranar Idil Ghadir.
Kira, buƙata da roko na gare ku masoya shi ne cewa a cikin dama mai kyau, tare da cewa a ranar Ghadir Khum kuna karanta wannan ziyara da aka samo daga Imam Hadi (A.S), ku kula da sassan ta.
Wannan ziyara, wani babi ne na bitar tarihin Musulunci da abubuwan da suka faru a farkon Musulunci, kuma babi ne na nazarin darajoji da falalolin Ali bin Abi Talib (A.S) da aka bayyana daga harshen Imam ma'asumi.
Ina fatan Ubangiji madaukaki ya sanya wannan biki mai albarka na Ghadir ya kasance mai albarka a kanmu baki daya, kuma ya tabbatar da Wilaya wacce take da makami mai karya makiya, a matsayin cikakkiyar ni'ima a wannan kasa da kuma a cikin al'ummar Musulmi.
Haka kuma ya ba al'ummarmu nasarar da za su sabunta alkawarin da suka kulla da Wilaya; da Wilayar A'imma (A.S), da Wilayatul Faƙih, da marigayi Imam dinmu da Imam dinmu shahidi, kamar yadda aka kulla alkawarin Ghadir Khum, kuma su kasance masu tsayin daka a kansa.
Ya Allah ka sanya mu cikin sahabbai da masoyan Ali (A.S) kuma ka sanya bikin Ghadir ya kasance mai albarka a kanmu baki daya, kuma ka yi mana kyauta da gaggauta bayyanar Imamuz Zaman (A.F).
Barka da wannan rana ga dukkan mabiya da masoyan Ali (A.S).
Wassalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuhu.
Ra'ayinka